Ƙungiyar tsaron Saudiyya Pakista da Turkiyya sun gana a karon farko

Asalin hoton, Burak Kara/Getty Images
Ministocin harkokin waje da manyan jami’an tsaro daga Turkiyya, Saudiyya da Pakistan sun taru a Istanbul a ranar Litinin, 31 ga Agusta, domin halartar taron farko na wani kwamitin da aka kafa a ƙarƙashin Yarjejeniyar Tsaro ta Makka.
Daga cikin jami’an da suka halarci taron akwai Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan, Ministan Harkokin Wajen Saudiyya Faisal bin Farhan Al Saud, Ministan Harkokin Wajen Pakistan Muhammad Ishaq Dar, Ministan Tsaron Saudiyya Yarima Khalid bin Salman, Babban Hafsan Sojin Pakistan Field Marshal Asim Munir, Babban Hafsan Sojin Turkiyya Janar Selçuk Bayraktaroğlu, da Ministan Tsaron Pakistan Khawaja Muhammad Asif.
Kasashen nan uku masu rinjayen al’ummar Musulmi mabiya Sunni, wadanda ke kawance da Amurka, sun rattaba hannu kan Yarjejeniyar Tsaron Juna ta Makka kimanin makonni uku da suka gabata a birnin Makka na Saudiyya.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ce kasashen sun hada kai ne sakamakon damuwa kan yakin Iran da sauran rikice-rikicen yankin, ciki har da harba makaman linzami da Iran ta yi kan kasashen da ke fitar da man fetur a yankin Tekun Fasha.
An bayyana manufar Yarjejeniyar Tsaro ta Makka da cewa ita ce “ƙarfafa matakan kariya na bai ɗaya domin daƙile duk wani nau’in hari.” Kamar tanadin kariyar haɗin gwiwa da ke cikin Mataki na 5 na Yarjejeniyar NATO, yarjejeniyar ta tanadi cewa duk wani hari da aka kai wa ɗaya daga cikin waɗannan ƙasashe uku za a ɗauke shi tamkar hari ne kan dukkaninsu.
Wata majiya daga Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta shaida wa Reuters cewa “batutuwan da suka shafi tsaron ƙasa da ƙasa za su kasance cikin ajandar taron.”
Kara karantawa: Yarjejeniyar Makka; an gudanar da taron haɗin gwiwa na farko tsakanin Turkiyya, Pakistan da Saudiyya a Istanbul.

Asalin hoton, Burak Kara/Getty Images











































